Yadda zanga-zanga kan tsadar rayuwa ta sake barkewa a jihar Arewa


Wasu matasa a garin Suleja na jihar Neja sun mamaye kan tituna a ranar Laraba 7 ga watan Fabrairu don nuna damuwarsu saboda tsadar kayan abinci a jihar.


 Fusatattun matasan sun mamaye tituna suna kira ga gwamnatin shugaba Bola Tinubu da ta kawo karshen wahalhalu da hauhawar farashin kayayyaki da suke fama da su.


 “Akwai wata zanga-zanga da ke gudana a karamar hukumar Suleja ta jihar Neja.  Suna kira ga Tinubu da ya kawo karshen wahalhalun da talakawa ke fama da shi a kullum a kasar nan,” inji wani ganau


 A ranar Litinin, 5 ga watan Fabrairu, maza da mata da matasa a Minna babban birnin jihar Neja su ma sun gudanar da zanga-zangar nuna adawa da hauhawar farashin kayayyaki a kasar.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN