Kotu ta daure matar aure a Kano rai da rai bisa wani dalili daya


Wata babbar kotu a Kano karkashin jagorancin Mai shari’a Halima Sulaiman ta yanke wa wata matar aure Rukayya Abubakar hukuncin daurin rai-da-rai, bisa laifin kashe dan kishiyarta. Daily trust ta rahoto.


 Lauya mai shigar da kara, Barista Rabia Sa’ad, ta bayyana wa kotun cewa a shekarar 2021, Rukayya ta jefa yaron a cikin rijiya, lamarin da ya kai ga mutuwarsa.


 A cewar Sa’ad, laifin da wanda ake tuhumar ta aikata ya sabawa sashe na 221 na kundin laifuffuka.


 A yayin shari’ar, lauyan mai gabatar da kara ta gabatar da shaidu hudu a gaban kotun.


 Lauyan wanda ake kara, Barista Rilwan Muhammad, ya roki kotun da ta yi wa wacce yake karewa sassauci domin uwa ce mai ‘ya’ya da dama da take kula da su.


 Sai dai kotun ta umarci mai laifin da ta ci gaba da zama a gidan yari har tsawon rayuwarta a Duniya..

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN