Da duminsa: Yan sanda sun sheke kasurgumin dan bindiga Isa Dei-Dei a Abuja


Jami’an rundunar ‘yan sandan Najeriya sun yi nasarar kashe wani dan bindiga mai suna Isa Dei-Dei a babban birnin tarayya Abuja.


 Jami’in hulda da jama’a na rundunar, ACP Olumuyiwa Adejobi, wanda ya bayyana hakan a wata sanarwa a ranar Laraba, 7 ga watan Fabrairu, 2024, ya ce ‘yan sandan sun kai farmaki maboyar ‘yan fashin inda aka yi artabu mai tsanani.


An bindige Isa Dei-Dei har lahira yayin da ‘yan kungiyarsa suka tsere da raunukan harbin bindiga.


 “Da misalin karfe 1015 na HRS a ranar 5 ga watan Fabrairun 2024, jami’an DFI-IRT da ke aikin leken asiri, sun samu bayanai kan maboyar wasu ‘yan bindiga da suka yi kaurin suna a unguwar da ke cikin babban birnin tarayya Abuja, karkashin jagorancin wani Isa Dei-Dei kuma nan take jami'an suka je wurin wurin don su kama shi,” in ji sanarwar.


 “Da suka hangi ‘yan sandan sai suka gudu, nan take jami’an suka bi su, lamarin da ya kai ga musanyar harbin bindiga mai zafi, ana cikin haka ne aka kashe fitaccen dan bindiga Isa Dei-Dei, yayin da sauran ’yan kungiyar suka yi nasarar tserewa.  tare da raunukan harbin bindiga a jikinsu.


 “Don haka muna kira ga jama’a musamman ma’aikatan lafiya da su ja hankalinmu ga duk wanda aka gani da raunin harbin bindiga domin ci gaba da bincike.”

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN