SANARWA: Hukumar Hisbah jihar Kebbi na cigiyar wannan yaro mai suna Abdurrahaman


Hukumar Hisbah ta jihar Kebbi ta wallafa sanarwar cigiyar wannan yaro mai suna Abdurrahaman dan Unguwar Kofar Kola a garin Birnin kebbi. Suna cigiyar wannan yaro wanda yake da matsalar Jinnu kuma ya bar gida watanni uku da suka gabata ba labarinsa.

Hisbah ta wallafa cewa:

"A madadin uwayen wannan yaron Mai suna Abdurrahman, Dan garin Birnin Kebbi ta jihar kebbi a unguwar kofar kola, suna Bada cigayar sa yabar gida kusan wata 3 ba labarinsa Abdurrahman Yana fama da matsalar jinnu yasha su tafi dashi jihohi da dama daga baya a gansa 

A wannan karon ya kwashe tsawon wata 3 ba shi ba labarin sa, wani lokaci Bai magana ko ya fadi gari ko unguwar da ba tasu ba Don haka Ake rokon jama'a dasu taimaka da duk Wanda Allah yassa yagamshi ko yaji labarinsa a sanar da hukumar Hisbah ta jihar kebbi ko fadar Amiru zoramawa Alh bello Ibrahim Nahaliku ko wata hukuma Mafi kusa ko a tuntubi mahaifiyarsa a unguwar kofar kola dake Nan Birnin Kebbi jama'a ataimaka Muna da sharing ko Allah zaisa adace 

Allah ya sa adace ameen"

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN