Kakakin hukumar ta NAF, Air Vice Marshall, Edward Gabkwet, ya ce an kashe Janari da makarraban sa ne a ranar Alhamis, 18 ga watan Janairu, a wani wuri kusa da Gadar Katako a karamar hukumar Igabi.
Ana zarginsu da kai hare-hare da sace-sace da dama a cikin jihar Kaduna da kuma kan hanyar Abuja zuwa Kaduna. An ba da izinin kai hare-hare ta sama bayan da aka ga Janari da ‘yan kungiyarsa a wani wuri kusa da Gadar Katako a karamar hukumar Igabi a jihar Kaduna.
Sanarwar ta ce;
“Bayan bayanan da aka samu sun nuna cewa lallai an kawar da Janari tare da wasu ‘yan ta’adda/ masu garkuwa da mutane da dama.
“An kuma kai irin wannan harin ta sama a ranar 20 ga watan Janairun 2024 akan maboyar ‘yan ta’adda da masu garkuwa da mutane a kusa da Chukuba a jihar Neja tare da samun nasarori daban-daban.
"Bayanai da aka samu bayan hare-haren ya nuna cewa bayan halaka Yan ta'addan, an kuma lalata karfinsu na motsi da ababen hawansu.."
From ISYAKU.COM