Awanni kadan bayan dakatar da ita, Ministar Tinubu ta sha kunya a fadar Aso Rock, dalili ya bayyana


Dakatacciyar Ministar jin kai da walwala, Dakta Betta Edu ta sha kunya bayan hana ta shiga wurin Tinubu. Legit Hausa ya wallafa.

Edu ta zo fadar shugaban kasar ce a Abuja jim kadan bayan an dakatar da ita inda ta ke neman ganawa da shugaban, cewar Tribune.

Yayin da ta wuce dukkan shingayen jami'an tsaro, an dakatar ta ita daga ganin Shugaba Tinubu a cikin ofishinsa.

Har ila yau, bayan an hana ta ganin shugaban, jami'an tsaron sun kuma kwace katin shaidar shiga fadar daga gare ta.

Daga bisani kuma jami'an tsaro sun fitar da ita daga fadar a cikin wata mota kirar Toyota Hilux ta fadar Aso Rock.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN