Tafka sata a cikin Masallaci, an tilasta barawon cin danyen barkono


An kama wani fitaccen barawo da ake zargin ya kware wajen sata a Masallatai a birnin Mombasa na kasar Kenya, tare da tilasta masa cin danyen barkono.


 A cewar mawallafin yanar gizo na kasar Kenya, Cyprian Nyakundi, an kama wanda ake zargin a Masallacin Mkanyageni ranar Talata, 26 ga Disamba, 2023.


 “An kama shahararren barawo mai suna Wa Viatu a Masallatai daban-daban a Mombasa babban birnin kasar Kenya.  Jiya an kama shi dumu-dumu a Masallacin harin Mkanyageni kuma hukuncin da aka yi masa ya kunshi duka da tilasta shi cin danyen barkono,” ya rubuta.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN