Musabbabin mutuwar Gwamnan Ondo ya bayyana

 

Gwamnatin jihar Ondo ta bayyana musabbabin mutuwar gwamna Rotimi Akeredolu.

 Gwamnatin jihar ta kuma sanar da cewa gwamnan bai mutu ba a Legas kamar yadda aka ruwaito.

 Akeredolu ya rasu ne a ranar Laraba, 27 ga Disamba, 2023, yana da shekaru 67.

 An yi ta yada cewa gwamnan ya rasu ne a wani asibitin Legas bayan ya sha fama da ciwon daji, da kuma cutar sankarar jini.

 Sai dai kwamishinan yada labarai da wayar da kan jama’a na jihar Ondo, Bamidele Ademola-Olateju, a wata sanarwa da ya fitar ranar Laraba, ya bayyana yadda gwamnan ya rasu.

 Yace;  "Akeredolu ya rasu ne yayin da yake jinya a Jamus.  Ya fuskanci matsalolin da suka taso daga ciwon daji na prostate.

 "Iyalan da gwamnatin jihar za su fitar da karin bayani game da shirye-shiryen jana'izarsa."

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN