An gano gawar wani mutum wanda ba a san ko waye ba an kone ta a Unguwar Takita a Birnin kebbi


An gan gawar wani mutum da ba a san ko waye ba an kona shi a shiyyar Takita da ke bayan unguwan Oando a garin Birnin kebbi. Hukumar Hisbah ta jihar Kebbi ta sanar da haka ranar Laraba 20/12/2023.

Hukumar ta wallafa cewa:


"ANGA GAWAR WANI MUTUN KONANNA WANDA  BA A SAN KO WANENE BA SHIYAR TAKITA BAYAN OANDO GARIN BIRNIN KEBBI

Ansamu rahoton cewar an kashe wani mutun Kuma an konashi a takita bayan oando garin Birnin Kebbi 

Ana sa ran ankashe shi fiye da kwana biyu da suka gabata Amma ba a sanar da hukuma ba sai yau laraba 20/12/2023 bayan jikin sa ya lalace  kawo yanzu baa iya tantance sanadiyar mutuwar wannan bawan Allah 

Bincike Yana kan gudana Don gano musabbabin wannan dayen aikin"

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN