An bizine gawar da aka kashe aka koneta a Sakita da ke bayan Oando Birnin kebbi


An bizine gawar da aka kashe aka kone ta a shiyar Sakita da ke Unguwar bayan Oando a garin Birnin kebbi.

Jami'an hukumar Hisbah na jihar Kebbi suka jagoranci jana'izar gawar bisa abin da ya sauwaka na ka'idodin addinin Musulunci duba da gawar ta fara rubewa har ta farawa wari.

Bayanai sun yi nuni da cewa ana kyautata zaton an kashe gawar ne kwanaki uku da suka gabata kafin a koneta.

Har zuwa lokacin binne gawar ranar Alhamis 21/12/2023 babu wanda ya shada gawar balle dalilin da ya sa aka kasheta.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN