'Yan bindiga sun sace sama da mutane 100 a Zamfara saboda rashin biyan harajin N50m


'Yan ta'adda sun sama da mutane 100 a garin Mutunji da ke karamar hukumar Maru a jihar Zamfara a arewa maso yammacin Najeriya.

 An tattaro cewa ‘yan ta’addan (’yan bindiga) sun kai harin ne a daren Juma’a bayan sallar isha’i. PM News ta rahoto.

 Mazauna yankin sun shaida wa Sashen Hausa na BBC cewa ‘yan bindigar sun kasance masu biyayya ga Damina, dan ta’addan da ke yankin.  Sun ce ‘yan bindigar sun zo ne a kan babura inda suka kewaye mutanen kauyen kafin su kai su dajin.

 An gano cewa an sace su ne saboda rashin biyan harajin Naira miliyan 50 da mutanen kauyen za su ba Damina.

 Babu wata sanarwa daga jami'an tsaro game da harin da aka kai a daren Juma'a a garin Mutunzi kawo lokacin rubuta wannan rahotu.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN