Sojoji sun ceto mutane 6 da aka yi garkuwa da su a jihar Kebbi

 

Dakarun sojojin Najeriya da 'yan banga sun ceto wasu mutane shida da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su a dajin da ke karamar hukumar Shanga a jihar Kebbi ranar Juma'a.

 Malam Yahaya Sarki, mai ba Gwamna Nasir Idris shawara na musamman kan harkokin yada labarai da wayar da kan jama’a ne ya bayyana haka a Birnin Kebbi a ranar Asabar din da ta gabata, inda ya ce an kubutar da dukkan wadanda aka yi garkuwa da su cikin koshin lafiya kuma an dawo da su ga iyalansu.

 “Dakarun Bataliya 1, Dukku Barrack, Birnin Kebbi tare da ‘yan banga sun kai farmaki tsaunin Kogon Damisa da ke kusa da Saminaka a karamar hukumar Shanga, kan iyaka tsakanin Kebbi da Neja a ranar Juma’a.

 “Rundunar ta fatattaki ‘yan bindiga da dama tare da ceto mutane shida da aka yi garkuwa da su.

 “An riga an ba da rahoton bacewar wadanda abin ya shafa, yayin da aka sace su da dadewa,” in ji shi.

 Sarki ya yabawa kwazon sojojin tare da jaddada kudirin gwamnati na tallafawa hukumomin tsaro a jihar. 


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN