Yadda dan gudun hijira mai shekara 53 ya taushe karamar yarinya mai tabin hankali ya yi mata fyade


An kama wani mutum mai shekaru 53 mai suna Usman Tela Ahmadu, dan gudun hijira (IDP) da ke zaune a garin Samunaka a karamar hukumar Yola ta Arewa bisa laifin yin lalata da wata karamar yarinya mai tabin hankali.

 Wanda ake zargin dan asalin garin Maiduguri ne a jihar Borno, rahotanni sun ce yana samun kyautuka da tallafin da bai kamata ba daga mazauna yankin.

 A cewar ikirari daga wanda ake zargin, ya yi lalata da yarinyar da ke fama da tabin hankali har sau hudu tun farkon shekarar 2021.

 Kwamishinan ‘yan sandan jihar, CP Afolabi Babatola, ya nuna damuwarsa da faruwar lamarin, ya kuma yi kira ga iyaye da masu kula da su da su samar da kayayyakin bukatu ga yaransu don hana su fadawa hannun masu aikata laifuka.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN