Illustrative picture |
Babban Khadi na Jihar Kano, Dokta Tijjani Ibrahim-Yakasai, ya kafa wani kwamiti da zai duba shari’ar wani dattijo da ke jiran yanke masa hannu na tsawon shekaru 18 a gidan yari.
Ibrahim-Yakasai ya kuma bayar da belin wasu mutane 147 da suka aikata kananan laifuka a wasu cibiyoyin tsare mutane guda biyu a jihar.
Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da SC Musbahu Kofar-Nassarawa, mai magana da yawun hukumar gyara hali ta Kano, SC Musbahu Kofar-Nassarawa, ya fitar ranar Litinin a Kano.
Ya ce an yanke shawarar ne don rage cunkoso a cibiyoyin da ake tsare da su a jihar.
A cewarsa, kwamitin ya kunshi alkalai shida kuma yana karkashin Alkalin Kotun Shari’ar Musulunci, Malam Ibrahim Sarki-Yola.
“A baya dai wata kotun shari’ar Musulunci ta Kano ta bayar da umarnin yanke kafar hagu da hannun daman wanda ake tuhuma a hukuncin da ta yanke kan aikata laifin sata.
"Kwamitin zai duba shari'ar zaman gidan yari na tsawon shekaru 18 a Kano da mutumin ya yi ba tare da zartar da hukuncin ba."
Ibrahim-Yakasai ya bukaci fursunonin da aka sako da su kasance masu hali na hari da kuma nisantar duk wani nau'i na rashin da'a da zai iya mayar da su wurin gyara hali kuma.
From ISYAKU.COM