Shekara 18 bayan hukuncin yanke masa kafar hagu da hannun dama a Kano saboda laifin sata...

 
Illustrative picture

Babban Khadi na Jihar Kano, Dokta Tijjani Ibrahim-Yakasai, ya kafa wani kwamiti da zai duba shari’ar wani dattijo da ke jiran yanke masa hannu na tsawon shekaru 18 a gidan yari.

 Ibrahim-Yakasai ya kuma bayar da belin wasu mutane 147 da suka aikata kananan laifuka a wasu cibiyoyin tsare mutane guda biyu a jihar.

 Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da SC Musbahu Kofar-Nassarawa, mai magana da yawun hukumar gyara hali ta Kano, SC Musbahu Kofar-Nassarawa, ya fitar ranar Litinin a Kano.

 Ya ce an yanke shawarar ne don rage cunkoso a cibiyoyin da ake tsare da su a jihar.

 A cewarsa, kwamitin ya kunshi alkalai shida kuma yana karkashin Alkalin Kotun Shari’ar Musulunci, Malam Ibrahim Sarki-Yola.

 “A baya dai wata kotun shari’ar Musulunci ta Kano ta bayar da umarnin yanke kafar hagu da hannun daman wanda ake tuhuma a hukuncin da ta yanke kan aikata laifin sata.


 Ibrahim-Yakasai ya bukaci fursunonin da aka sako da su kasance masu hali na hari da kuma nisantar duk wani nau'i na rashin da'a da zai iya mayar da su wurin  gyara hali kuma.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN