Yan binduga sun sake kutsa fada don sace Sarkin Maru, basu sameshi ba sun afka gidaje wajen neman shi sun kashe mutum 4


Mutane hudu sun mutu bayan wasu ‘yan bindiga sun kai musu hari a garin Maru na jihar Zamfara.


 Idan ba a manta ba a ranar Talata 24 ga watan Oktoba ne wasu ‘yan bindiga suka kai hari fadar  Sarkin Maru, Abubakar Maigari da ke karamar hukumar Maru a jihar, inda ‘yan sanda suka dakile harin.


 Abin baÆ™in ciki, an kashe mutum É—aya.  Marigayin dai an bayyana sunan sa da Malam Ukashatu, wani mutum ne da ke zaune a gefen fadar.


 ‘Yan fashin sun kuma yi awon gaba da wani jami’in IT.


 Sannan kuma a daren Alhamis, 26 ga watan Oktoba, an ce ‘yan ta’addan sun koma fadar domin neman sarkin.


 Ba su same shi ba sai suka afkawa gidaje a unguwar suna nemansa inda suka kashe mutum hudu a cikin lamarin.


 A yau 27 ga watan Oktoba ne aka gudanar da sallar jana'izar wadanda suka mutu kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN