Yan binduga sun sake kutsa fada don sace Sarkin Maru, basu sameshi ba sun afka gidaje wajen neman shi sun kashe mutum 4


Mutane hudu sun mutu bayan wasu ‘yan bindiga sun kai musu hari a garin Maru na jihar Zamfara.


 Idan ba a manta ba a ranar Talata 24 ga watan Oktoba ne wasu ‘yan bindiga suka kai hari fadar  Sarkin Maru, Abubakar Maigari da ke karamar hukumar Maru a jihar, inda ‘yan sanda suka dakile harin.


 Abin baÆ™in ciki, an kashe mutum É—aya.  Marigayin dai an bayyana sunan sa da Malam Ukashatu, wani mutum ne da ke zaune a gefen fadar.


 ‘Yan fashin sun kuma yi awon gaba da wani jami’in IT.


 Sannan kuma a daren Alhamis, 26 ga watan Oktoba, an ce ‘yan ta’addan sun koma fadar domin neman sarkin.


 Ba su same shi ba sai suka afkawa gidaje a unguwar suna nemansa inda suka kashe mutum hudu a cikin lamarin.


 A yau 27 ga watan Oktoba ne aka gudanar da sallar jana'izar wadanda suka mutu kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.


Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN