Malamin addini ya mutu nan take bayan ginin wajen ibada ya ruguje yayin da yake gudanar da addu'a


Wani Fasto ya mutu bayan da wani ginin Cocin Dunamis da ke ofishin Ward North Bank a Makurdi, babban birnin jihar Benue ya ruguje da sanyin safiyar ranar Talata, 3 ga watan Oktoba.


 Rahotanni sun bayyana cewa limamin cocin tare da wasu mutane na gudanar da addu'o'i a ginin cocin a lokacin da ya ruguje.  Wasu mutane ukun da ke harabar cocin sun tsere da ransu.


 Gine-ginen gidaje da kayayyakin wutar lantarki da ke kewayen ginin sun ruguje.

Kawo yanzu ba a san musabbabin faruwar lamarin ba.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN