Duba ɗan jigon PDP mai shekaru 24, da Tinubu ya naɗa a matsayin shugaban FERMA


Shugaba Bola Tinubu ya nada sabon shugaban hukumar gudanarwa na hukumar kula da hanyoyin tarayya (FERMA) na tsawon shekaru hudu.

 Sabon shugaban FERMA da aka nada, Engr.  Imam Ibrahim Kashim Imam ya zama mafi karancin shekaru da Tinubu ya nada matsayin jagoranci tun bayan rantsar da shi a matsayin Shugaban Najeriya. Legit.ng ya wallafa.

An yaba wa shugaba Tinubu saboda nada matasa da yawa cikin majalisarsa.  A baya dai ya yi alkawarin cewa matasan za su taimaka wa gwamnatin sa.

Engr.  Imam Ibrahim Kashim Imam matashi ne dan shekara 24 da haihuwa, an haife shi a watan Disambar 1998. Ya kammala karatunsa a jami'ar Brighton da ke kasar Burtaniya inda ya yi digiri na farko a fannin injiniya.

 Matashin mai farin jini ya samu digirinsa na farko da na biyu a Jami’ar Brighton kuma ya kammala bautar kasa (NYSC) a watan Agustan 2022.

 Kafin nadin nasa da shugaba Tinubu yayi, Imam Muhammed ya kasance mataimaki na musamman ga ministan ayyuka kuma tsohon gwamnan jihar Ebonyi, Dave Umahi.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN