Boko Haram sun halaka babban limamin Masallacin Juma'a a Borno, sun kone litattafansa na ilimi


Wasu da ake zargin mayakan Boko Haram ne sun kashe Sheikh Baba Goni Muktar Malumti, babban limamin masallacin Jumat na tsakiyar garin Benisheikh, hedikwatar karamar hukumar Kaga a jihar Borno.


 An tattaro cewa ‘yan ta’addan da ke cikin wata mota Volkswagen sun kai farmaki gidan limamin da ke Malamti, a wajen garin Benisheikh da misalin karfe 12:30 na safiyar ranar Litinin, 30 ga Oktoba, 2023.


 'Yan ta'addan sun kuma kona wasu litattafai na marigayin.


 Imam kafin rasuwarsa ya kasance sanannen malamin addinin musulunci.


 A cewar wata majiyar rundunar hadin gwiwa ta Civilian Task Force, yanayin farmakin ya kasance na masu tada kayar baya ne.


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN