Wasu da ake zargin mayakan Boko Haram ne sun kashe Sheikh Baba Goni Muktar Malumti, babban limamin masallacin Jumat na tsakiyar garin Benisheikh, hedikwatar karamar hukumar Kaga a jihar Borno.
An tattaro cewa ‘yan ta’addan da ke cikin wata mota Volkswagen sun kai farmaki gidan limamin da ke Malamti, a wajen garin Benisheikh da misalin karfe 12:30 na safiyar ranar Litinin, 30 ga Oktoba, 2023.
'Yan ta'addan sun kuma kona wasu litattafai na marigayin.
Imam kafin rasuwarsa ya kasance sanannen malamin addinin musulunci.
A cewar wata majiyar rundunar hadin gwiwa ta Civilian Task Force, yanayin farmakin ya kasance na masu tada kayar baya ne.