An yi wa Malamar jami'ar FUTMinna yankan rago a gidanta a birnin Minna jihar Neja


An tsinci gawar wata malamar Sashen Biochemistry na Makarantar Kimiyyar Rayuwa ta Jami’ar Fasaha ta Tarayya (FUT) Minna a Jihar Neja, Dokta (Mrs) Adefolalu Funmilola Sherifat da aka yanka a gidanta da ke Unguwar Gbaiko a garin. Shafin labarai na yanar gizo isyaku.com ya samo.


 Channels TV ta ruwaito cewa shugaban kungiyar malaman jami’a (ASUU) a makarantar Farfesa Gbolahan Bolarin ya ce ,an gano gawar marigayiyar ne a safiyar Lahadi, 29 ga watan Oktoba, lokacin da mabiya cocin ta suka bi ta gidanta bayan ba a gan ta a lokacin hidimar ibada ba.


 Wasu mazauna garin sun ce bayan da aka bude kofar gidanta, an same ta a cikin jininta kuma an yi mata yankan rago a makogwaronta da wukake a gefenta.  Daga baya hukumomin ‘yan sanda sun dauke gawar zuwa dakin ajiyar gawa.


 Kafin rasuwarta, tana zaune tare da wata mai yi mata hidima, amma ta sallami yarinyar a ranar Juma’a, 27 ga Oktoba.


 Har yanzu rundunar ‘yan sandan jihar Neja ba ta tabbatar da faruwar lamarin ba kafin lokacin rubuta wannan rahotu.


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN