Da duminsa: Yan sanda sun kama yan uwan juna guda biyu bisa zargin kisan dan Jaridar jihar arewa

 

Wasu ’yan uwa biyu suna tsare a ofishin ‘yan sanda na Tudun Wada da ke garin Gusau a Jihar Zamfara, bisa zargin kashe wani wakilin Muryar Najeriya, Hamisu Danjigba
.


 Wadanda ake zargin, Bilal Haruna da, Mansur Haruna, ‘ya’yan yayan marigayi Danjigba ne, Malam Haruna.


 Suna zaune ne a gidan marigayi Danjigba da ke unguwar Samaru a birnin Gusau, kafin kisan.


 Danjigba, wanda aka bayyana bacewarsa a ranar Asabar, 16 ga watan Satumba, ya koka a lokuta da dama kan rashin da'a na mutanen biyu, wadanda 'yan uwansa ne.


 Bayan ya bace ne aka aika da sako ga iyalansa.  A sakon text na wayar salula, wanda ya aika ya bukaci N1m a matsayin wani bangare kafin a bayyana kudin fansa na karshe ranar Juma'a.


 Abin baÆ™in ciki, an tsinci gawarsa a ranar Laraba, 20 ga Satumba, an jefar da shi a wani laka a bayan gidansa.


  An kama ‘yan uwansa dangane da kisan nasa, yayin da ake ci gaba da bincike kan lamarin.


 Danjigba yayi aiki a gidajen yada labarai da dama kamar, Jaridar Ayau, Kunnen Gari, Muryar Najeriya da FM Nigeria.


 Ya rasu ya bar mata da ‘ya’ya da jikoki.


Published by isyaku.com
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN