Da duminsa: Yan sanda sun kama yan uwan juna guda biyu bisa zargin kisan dan Jaridar jihar arewa

 

Wasu ’yan uwa biyu suna tsare a ofishin ‘yan sanda na Tudun Wada da ke garin Gusau a Jihar Zamfara, bisa zargin kashe wani wakilin Muryar Najeriya, Hamisu Danjigba
.


 Wadanda ake zargin, Bilal Haruna da, Mansur Haruna, ‘ya’yan yayan marigayi Danjigba ne, Malam Haruna.


 Suna zaune ne a gidan marigayi Danjigba da ke unguwar Samaru a birnin Gusau, kafin kisan.


 Danjigba, wanda aka bayyana bacewarsa a ranar Asabar, 16 ga watan Satumba, ya koka a lokuta da dama kan rashin da'a na mutanen biyu, wadanda 'yan uwansa ne.


 Bayan ya bace ne aka aika da sako ga iyalansa.  A sakon text na wayar salula, wanda ya aika ya bukaci N1m a matsayin wani bangare kafin a bayyana kudin fansa na karshe ranar Juma'a.


 Abin baÆ™in ciki, an tsinci gawarsa a ranar Laraba, 20 ga Satumba, an jefar da shi a wani laka a bayan gidansa.


  An kama ‘yan uwansa dangane da kisan nasa, yayin da ake ci gaba da bincike kan lamarin.


 Danjigba yayi aiki a gidajen yada labarai da dama kamar, Jaridar Ayau, Kunnen Gari, Muryar Najeriya da FM Nigeria.


 Ya rasu ya bar mata da ‘ya’ya da jikoki.


Published by isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN