Da duminsa: Yan sanda sun cafke wadanda suka kashe mai POS suka dauke masa N3.5m da rana tsaka

 

Rundunar ‘yan sandan jihar Ekiti ta kama wasu mutane 13 da ake zargin ‘yan kungiyar asiri ne da suka kashe wani ma’aikacin POS mai suna Olasunkanmi Joseph tare da kwashe masa kudi N3.5m a Ado-Ekiti.


 Ku tuna cewa an kashe Olasunkanmi a Irona Roundabout da ke Ado Ekiti da rana tsaka a ranar Alhamis, 6 ga Afrilu, 2023, yayin da yake dawowa daga banki.


 An gabatar da wadanda ake zargin ne a hedikwatar rundunar a karshen mako tare da wasu mutane 16 da aka kama bisa zargin aikata laifuka daban-daban kamar su garkuwa da mutane, da kuma yunkurin kisa.

 Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Sunday Abutu, ya ce an kama wadanda ake zargin ‘yan kungiyar asiri ne bayan da aka samu labarin cewa suna shirin sake kai wani harin fashi da makami daga maboyar su.


 Wadanda ake zargin sun amsa laifinsu na kasancewa mambobin kungiyar asiri ta Supreme Eiye Confraternity a Ikere-Ekiti kuma suna da hannu wajen kai hare-hare na fashi da kuma garkuwa da mutane.


 A cewar PPRO, bindigar AK-47 da aka samu daga hannun wadanda ake zargin na daga cikin makaman da aka yi amfani da su wajen kashe ma’aikacin POS.


Published by isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN