Dubu ta cika: An kama kasurgumin barawon da ya fasa shago ya yi awon gaba da wayar salula 996, laptap 9 da sauransu..


Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta kama wasu mutane biyar da ake zargin barayi ne tare da kwato wayoyin hannu guda 996 da aka sace, da kwamfutocin tafi da gidanka guda tara da katin ATM da dai sauransu
.

 Kakakin rundunar ‘yan sandan, ,SP Abdullahi Haruna Kiyawa, wanda ya bayyana hakan a wata sanarwa a ranar Talata, 26 ga Satumba, 2023, ya ce daya daga cikin wadanda ake zargin Ibrahim Adamu ya fasa shaguna goma sha daya a Kasuwar GSM ta Dansulaika inda suka yi awon gaba da wayoyin hannu, teburi, kwamfutocin tafi da gidanka.  da wasu kudaden tallace-tallace.


 Wata tawagar ‘yan sanda ta kaddamar da wani samame karkashin jagorancin jami’an leken asiri, inda ta kai ga cafke wanda ake zargin a unguwar Sallari da ke karamar hukumar Tarauni a jihar.

 Adamu ya amsa laifin aikata laifin ne shi kadai, sannan ya jagoranci jami’an tsaro wajen kwato kayayyakin da aka sace da suka hada da wayoyin hannu guda 106.


Published by isyaku.com
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN