DA DUMI-DUMI: Yan bindiga sun harbe daliban Nasarawa Poly 3, sun yi garkuwa da wata daliba


  Rahotanni sun bayyana cewa wasu ‘yan bindiga sun harbe wasu dalibai uku na kwalejin kimiyya da fasaha ta Isa Mustapha Agwai l da ke garin Lafiya a jihar Nasarawa. Daily trust ta rahoto.

 An tattaro cewa maharan sun kuma yi awon gaba da wata daliba guda daya da aka bayyana sunanta da Ajoke, dalibar ND ll a fannin fasahar kimiyya.

 Daily trust ta gano cewa lamarin ya faru ne da misalin karfe 08:00 na daren ranar Litinin.

 Daliban da suka samu raunuka harbin bindiga, an ce suna karbar magani a asibiti.


Published by isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN