Babbar magana: Uwagida ta siyo sabon wuka ta ce za ta sabunta wa maigida kaciya a Kano, gogan ya ruga zuwa Kotu



Wani magidanci mai suna Malam Ali, ya garzaya kotun shari'ar Muslunci da ke zamanta a rijiyar Lemo, don neman dakatar da matarsa daga iƙirarin sabunta ma sa kaciya da ta yi. Shafin legit Hausa ya wallafa
.

Ya shaidawa kotun cewa matar ta sa ta dade tana faɗa ma sa cewa za ta yi ma sa kaciya, inda a yanzu haka ma ya ce ta sayo wuƙa mai kaifi don cika aniyarta kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

Mijin, wanda ya kasance mata biyu gareshi, ya bayyana cewa tun ranar da ta yi wannan iƙirarin ya daina barci da idanu biyu a duk lokacin da zai kwana gidanta.

Alƙalin da ke kula da koken da aka shigar Malam Sunusi Danbaba Daurawa, ya ɗage sauraron ƙarar har zuwa ranar 4 ga watan Oktoba.

Da yake zantawa da manema labarai jim kaɗan bayan ɗage sauraron ƙarar, mijin ya bayyana cewa yanzu haka dai ya yi nasarar ɗauke wukar daga ɗakin matar ta sa, sai dai har yanzu hankalinsa bai kwanta ba.


Malam Ali ya kuma bayyana cewa bai san dalilin da ya sa matar ta sa ta yi hakan ba, saboda a cewarsa suna zaune lami-lafiya da ita.

Ya ƙara da cewa yana matuƙar ƙaunar matarsa, amma kuma ga abinda take shirin aikatawa, wanda ya sanyi shi kawo ƙararta gaban kuliya domin a tsayar da ita.

Manema labarai da suka yi kokarin jin ta bakin wannan mata kan abinda take shirin aikatawa, taki yadda ta yi hira da su.
Published by isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN