Yanzu yanzu: Rahotanni sun bayyana cewa Tinubu yana tunanin maida ‘tallafin man fetur na dan lokaci’


Rahotanni sun bayyana cewa shugaba Bola Tinubu na tunanin bayar da tallafin danyen man fetur na wucin gadi yayin da farashin danyen mai da kuma farashin kudaden waje ke ci gaba da hauhawa.


 Majiyoyin fadar shugaban kasa sun shaidawa TheCable cewa, shawarar tana kan teburi kuma “ainihin” adadin man fetur da ake sha a kasar yanzu an san shi bayan cire tallafin jim kadan bayan kaddamar da Tinubu.  Ɗaya daga cikin majiyoyin sun lura cewa adadin da aka kashe akan tallafi "a yanzu ana iya sarrafa shi".


 Hakan na zuwa ne bayan da Kamfanin Mai na Najeriya (NNPC) Limited ya ce babu wani shiri na kara farashin man fetir duk da tashin farashin danyen mai, tsadar rayuwa, da faduwar darajar Naira.


Published by isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN