Ta faru: Kurtun dan sanda ya bindige sajen har lahira wajen aikin sintiri


An kaddamar da bincike kan kisan wani babban jami'in 'yan sanda da karamin abokin aikinsa ya yi a karkashin wani yanayi da ba a tabbatar ba a yankin Nakuru na kasar Kenya.


 Kwamandan ‘yan sandan karamar hukumar Nakuru Samuel Ndanyi ya tabbatar da cewa wanda ake zargi, dan sanda Jackson Ndonga ya harbe Christopher Kimeli har lahira a lokacin da yake a hedikwatar yankin K9 na Rift Valley da ke yankin Gabashin Nakuru a safiyar ranar Talata 8 ga watan Agusta.


 Ndanyi ya ce;


 "Mun samu rahoto da misalin karfe 5 na safe daga wani dan sanda da ya ji karar harbin bindiga a cikin Sashen Kare, a wurin da lamarin ya faru, mun gano cewa wani karamin abokin aikinsa ya harbe jami'insa daya har lahira."


 Nan take aka kwance wa dan sandan makamai, kuma a halin yanzu yana tsare a babban ofishin ‘yan sanda na Nakuru.  Ana hasashen cewa mai yiwuwa dan sandan ya harbe sajan ne saboda rashin jituwa da ke tsakaninsu.  Rahoton 'yan sanda ya karanta;


 "Har yanzu ba a tabbatar da manufar jami'in ba, duk da haka, abokan aikinsu sun yi hasashen cewa Jackson Konga da Christopher Kimeli basu jituwa."

Published by isyaku.com
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN