Ƙungiyar raya tattalin arziƙin ƙasashen Afirika ta Yamma (ECOWAS) ta sake sanya sabbin takunkumi kan juyin mulkin da aka yi a Jamhuriyar Nijar.
Amma sojojin da suka yi juyin mulkin sun yi biris da barazanar ECOWAS sannan suka sha alwashin daƙile duk wani shiga tsakani daga ƙasar waje da za ayi a Nijar.
Da yake tattaunawa da manema labarai na fadar shugaban ƙasa a ranar Talata 8 ga watan Agusta, kakakin shugaban ƙasa, Ajuri Ngelale, ya bayyana cewa an ƙara sanya takunkumi akan masu hulɗa da sojojin da suka yi juyin mulki a Nijar, rahoton Daily Trust ya tabbatar.
Duk da dai bai yi cikakken bayani ba, ya bayyana cewa an yi hakan ne ta hannun babban bankin Najeriya (CBN).
Published by isyaku.com