An barni cikin duhu, ba mu’amala da mutane da cin busasshiyar shinkafa da taliya – hambararren shugaban Nijar Bazoum ya koka kan halin da yake ciki a tsare



Mohamed Bazoum, zababben shugaban kasar ta Nijar bisa tafarkin dimokuradiyya, ya ce gwamnatin mulkin soja da ta hambarar da shi ta tsare shi tare da tilasta masa cin busasshiyar shinkafa da taliya.


 A cikin jerin sakonnin text ga wani abokinsa da aka ruwaito CNN ta gani, Bazoum ya ce "an hana shi hulda da mutane" tun daga ranar Juma'a, Kuma aka hana ba shi abinci ko magani.


 Bazoum ya ce ya shafe mako guda yana rayuwa babu wutar lantarki, lamarin da ya zama ruwan dare ga daukacin 'yan Nijar bayan da Najeriya ta katse wutar lantarki sakamakon juyin mulkin.


 Bazoum ya ce duk abincin da aka kawo masa ya lalace, kuma yanzu yana cin busasshiyar taliya da shinkafa.


 Ko da yake masu juyin mulki sun ki tattaunawa da mukaddashin sakatariyar harkokin wajen Amurka Victoria Nuland a ziyarar da ta kai Yamai babban birnin Jamhuriyar Nijar a ranar Litinin, duk da haja Bazoum na tuntubar wasu kasashen waje.

Published by isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN