Matar aure ta kashe mijinta da wuka a Bauchi


Rundunar ‘yan sandan jihar Bauchi ta cafke wata mata mai suna Maimunatu Sulaiman ‘yar shekara 21 da haihuwa da laifin kashe mijinta da wuka a unguwar Kofar Dumi da ke jihar.

Mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar, ASP Aminu Gimba Ahmed, wanda ya bayyana hakan a wata sanarwa a ranar Juma’a, 7 ga watan Yuli, 2023, ya ce wanda ake zargin ta daba wa mijinta Aliyu Mohammad wuka a kirjinsa bayan wata hatsaniya ta barke a tsakaninsu.

PPRO ya ce lamarin ya faru ne a gidan ma’auratan a ranar Laraba, 5 ga watan Yuli, 2023, inda ya kara da cewa wacce ake zargin ta samu kananan raunuka a cikinta a lokacin fadan, ta amsa aikata laifin.

Published by isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN