Fusatattun mutane sun yi wa wasu matasa biyu ruwan duwatsu kan zargin satar babur


Wasu fusatattun jama’a sun kai hari kan wasu mutane biyu da ake zargin barayin babura ne, inda suka yi masu ruwan duwatsu a jihar Benue.


An tattaro cewa an kama wadanda ake zargin ne a lokacin da suke kokarin kwace babura daga hannun masu su a Gyado villa da ke Makurdi a yammacin ranar Alhamis, 6 ga watan Yuli, 2023.


Har yanzu babu cikakken bayani kan lamarin har zuwa lokacin da ake gabatar da wannan rahoto, sai dai wasu mazauna birnin da suka wallafa hotunan, sun yi kira ga ‘yan sanda da su kubutar da wanda ake zargin daga hannun mutanen da suka fusata.

Published by isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN