Kotu ta umurci Obasanjo, Yar’Adua, Jonathan da Gwamnonin Buhari da su yi bayani kan dala biliyan 5 da Abacha ya wawushe


Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta bayar da umarnin a bayyana yadda aka kashe kimanin dalar Amurka biliyan 5 da Abacha ya wawushe da gwamnatocin tsoffin shugabannin kasar Olusegun Obasanjo, Umaru Musa Yar’Adua, Goodluck Jonathan da Muhammadu Buhari suka kwato.

 Kotu ta umurci gwamnatin shugaba Bola Tinubu da ta bayyana ainihin adadin kudaden da Janar Sani Abacha ya wawure daga Najeriya, da jimillar kudaden da Abacha ya kwato da duk wata yarjejeniyoyin da gwamnatocin tsoffin shugabanni Obasanjo, da ‘Yar’adua suka sanya wa hannu a kai har da Jonathan da Buhari.”

Daily trust ta rahoto Mai shari’a James Kolawole Omotosho ne ya yanke hukuncin a makon da ya gabata, biyo bayan wata kara mai lamba FHC/ABJ/CS/407/2020, wadda kungiyar kare hakkin zamantakewa da tattalin arziki (SERAP) ta kawo.

A hukuncin da ya yanke, Mai shari’a Omotosho ya ce, “A karshe, bukatar da SERAP ta gabatar ya dace kuma gwamnatin tarayya ta ma’aikatar kudi ta bayar da umarnin mika wa SERAP cikakken bayanin kashe kimanin dala biliyan 5 da Abacha ya sace cikin kwanaki 7.  akan wannan hukuncin."

Published by isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN