An yi wa wasu yan mata bulala 40 saboda sanya tufafi da basu dace ba a wata al'umma


Wasu gungun matasa a yankin Ubeji da ke karamar hukumar Warri ta Kudu a jihar Delta, karkashin kungiyar matasan Ubeji Youth and Employment Development Organisation, sun yi kakkausar suka ga ‘yan matan da ke sanya suturar da ba ta dace
ba.

 A cewar jaridar Punch, mambobin kungiyar matasan sun fara danne wadanda ake zargi da aikata laifin ta hanyar yi musu bulala ko kuma a madadin sanya musu tara.

 An tattaro cewa aiwatar da atisayen mai lakabin ‘Yaki da sanya tufafin da ba su dace ba’ a tsakanin matasa mata a cikin al’umma, wanda ya fara tun ranar Litinin, 3 ga watan Yuli, 2023, ya haifar da firgici a tsakanin mata a yankin.

 Wasu daga cikin wadanda abin ya shafa, an ce an tilasta musu su biya tarar da ta kai Naira 10,000 ko kuma a yi musu bulala 40 da sanda.

 Sakataren kungiyar matasa Stanley Bomele, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya shaidawa manema labarai cewa " atisayen ya zama dole saboda yadda mata suke sanya tufafi a cikin al'umma."

 Ya kara da cewa, "Yawancin 'yan matan suna amfani da sunan saye-saye ne da sunan kwalliya inda wasunsu suka kusa yin tsiraici, abin da ke da ban haushi kuma ba ya yiwa al'umma dadi."

 Bomele ya danganta babban dalilin cin zarafin mata a yankin da sanya tufafin da bai dace ba ne a tsakanin 'yan mata.

 "Ba za a Æ™ara amincewa da saka riguna, guntun wando ko matsattsun wando ba daga Yan mata a cikin al'umma," in ji shi.

Published by isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN