Harin jirgin sama ya kashe mutane 22 a babban birnin Sudan



Wani hari da sojojin Sudan suka kai a babban birnin kasar ya kashe mutane akalla 22 tare da jikkata wasu da dama, kamar yadda shaidun gani da ido da wani jami'i suka sanar.

 Mata da yara na daga cikin wadanda abin ya shafa, kamar yadda shaidun gani da ido suka shaida wa BBC.

 An kai harin ta sama a yankin Dar es Salaam na Omdurman, daura da gabar kogin Nilu zuwa babban birnin kasar Khartoum, a safiyar ranar Asabar.

 Tun a watan Afrilu ne dai sojoji da dakarun sa-kai suke fafatawa don kwace babban birnin kasar.

 Rikicin dai ya faro ne bayan da shugaban rundunar sojin kasar Janar Abdel Fattah al-Burhan da kuma shugaban rundunar sojojin gaggawa ta RSF, Janar Mohamed Hamdan Dagalo suka yi takun-saka kan makomar kasar.

 Kamfanin dillancin labaran reuters ya nakalto wani jami’in kiwon lafiya na jihar Khartoum ya ce akalla mutane 22 ne suka mutu a harin na ranar Asabar, yayin da RSF ta ce adadin wadanda suka mutu ya kai 31.

Published by isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN