Gwamnati ta sanya dokar hana fita ta sa'o'i 24 a wata jihar Arewa


Gwamnan jihar Taraba, Agbu Kefas, ya sanya dokar hana fita ta sa’o’i 24 a garin Karim da kewaye sakamakon hare-haren da wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne suka kaddamar a wasu kauyukan karamar hukumar Karim Lamido.

 Sakataren yada labarai na gwamnan, Yusuf Sanda, a wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi, ya ce dokar hana fita ta biyo bayan sabon rikicin kabilanci a wasu sassan karamar hukumar Karim Lamido na jihar.

 Ya ce an wajabta wa jami’an tsaro da su tabbatar da bin doka da oda, kuma duk wani mutum ko gungun mutanen da aka samu sun karya wannan doka za a hukunta su kamar yadda doka ta tanada.

 Sanarwar ta umurci dukkan masu unguwanni, sarakunan gargajiya, da masu ruwa da tsaki a karamar hukumar Karim Lamido da su lura da dokar hana fita da gwamnatin jihar ta sanya.

Published by isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN