Dan bangan jihar Arewa ya auri wata ‘yar kasar Norway da ya hadu da ita a shafukan sada zumunta


Wani dan banga mai suna Hamman Joda Isa ya auri wata ‘yar kasar Norway mai suna Diana Maria Lugunborg a garin Yola da ke karamar hukumar Yola ta Arewa a jihar Adamawa. Shafin labarai na isyaku.com ya samo.

 An tattaro cewa Diana ta zo daga Norway kuma ta amince da auren Isa wanda ta hadu da shi a dandalin sada zumunta.

 Isah da Diana sun yi aure ne a babban ofishin rajistar babbar kotu da ke garin Yola kwanakin baya.

 Bayan haka an gudanar da liyafar daurin aure a wani wurin taron da ke daura da kwalejin koyon shari'a ta Yola.

Published by isyaku.com
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN