Dan bangan jihar Arewa ya auri wata ‘yar kasar Norway da ya hadu da ita a shafukan sada zumunta


Wani dan banga mai suna Hamman Joda Isa ya auri wata ‘yar kasar Norway mai suna Diana Maria Lugunborg a garin Yola da ke karamar hukumar Yola ta Arewa a jihar Adamawa. Shafin labarai na isyaku.com ya samo.

 An tattaro cewa Diana ta zo daga Norway kuma ta amince da auren Isa wanda ta hadu da shi a dandalin sada zumunta.

 Isah da Diana sun yi aure ne a babban ofishin rajistar babbar kotu da ke garin Yola kwanakin baya.

 Bayan haka an gudanar da liyafar daurin aure a wani wurin taron da ke daura da kwalejin koyon shari'a ta Yola.

Published by isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN