DA DUMI-DUMI: Ma'aikatan mai da aka sace sun sami 'yanci


 Ma’aikatan MRS Oil Nigeria Plc guda takwas da aka yi garkuwa da su a makon jiya a Legas sun samu ‘yanci, inji jaridar The Nation.

 An sako mutanen ne a daren Lahadi a unguwar Sangotedo da ke jihar Legas.

 Sai dai babu tabbas ko an biya kudin fansa don 'yancinsu.

 An sace ma’aikatan man ne da misalin karfe 6 na yammacin ranar Litinin yayin da suke cikin wani jirgin ruwa mai zaman kansa daga tsibirin Legas zuwa Lekki.

 An ce wadanda suka yi garkuwa da su sun shiga cikin kwale-kwalen da suke ciki, inda suka sace su suka bar kwale-kwalen ma’aikatan mai da kayansu a ciki.

 Kakakin Rundunar ’Yan sandan Legas, SP Benjamin Hundeyin, ya tabbatar wa jaridar The Nation sako ma’aikatan mai a safiyar ranar Litinin.

 Da aka tambaye shi ko an kama wadanda suka sace mutanen, Hundeyin ya mayar da martani da kakkausan harshe, inda ya ki karin bayani kan lamarin.

Published by isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN