An zaɓi Tinubu shugaban ƙungiyar Ecowas


Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya zama shugaban ƙungiyar Economic Community of West African States (Ecowas) ta ƙasashen Afirka ta Yamma. BBC Hausa ya wallafa.

Tinubu ya maye gurbin Shugaba Umaro Embalo na Guinea Bissau yayin taron da ƙasarsa ke karɓar baƙunci a yau Lahadi karo na 63.

"Za mu ɗauki dimokuraɗiyya da muhimmanci. Tana da wuya amma ita ce tsarin gwamnati mafi dacewa," a cewar Tinubu bayan an zaɓe shi a matsayin shugaban ƙungiyar.

Wannan ne taro na biyu da shugaban na Najeriya ke halarta a ƙasashen waje tun bayan da ya hau mulki a watan Mayu biyo bayan nasarar da ya yi a zaɓen watan Fabrairu.

Baya ga alwashin jagoranci na gari da ya ci, Tinubu ya bayyana damuwa kan yadda "matsalar tsaro da ta'addanci ke mayar da yankin Afirka ta Yamma baya".

Published by isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN