Yan sandan jihar Edo sun baro ta


Mukaddashin Sufeto-Janar na ‘yan sanda (IGP), Olukayode Adeolu Egbetokun, ya yi Allah-wadai da lamarin da ya tayar da hankulan jama’a inda tawagar ‘yan sanda suka bi ta kan wani dan Najeriya da mota a ranar Alhamis 29 ga watan Yuni, 2023 a Ekpoma, jihar Edo.

 Ya umurnin cewa a kawo yan sandan da ke tsare a jihar Edo hedikwatar rundunar ta Abuja a ranar Litinin domin ci gaba da daukar mataki. Jaridar The Nation to rahoto.

 A wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar, CSP Olumuyiwa Adejobi ya fitar a ranar Juma’a ya ce:

 “An yi kira ga jama’a musamman mutanen Ekpoma da su kwantar da hankalinsu domin shugabancin NPF mai ci ba zai lamunci irin wannan aiki na rashin da’a da saba doka ba.  ".

Published by isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN