Hukumomin Saudiyya sun kwashe alhazan Najeriya 10,000 zuwa sabbin tantuna

Nigerian pilgrims, Mahajjatan Najeriya


Hukumomin kasar Saudiyya sun amince da mayar da mahajjatan Najeriya kimanin 10,000 zuwa wani wurin da zai rage cunkoso a tantin da ke Muna.

 Malam Mousa Ubandawaki mataimakin daraktan yada labarai na hukumar alhazai ta kasa NAHCON ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a birnin Makkah ranar Litinin. PM News ta rahoto.

 Ubandawaki ya ce matakin wani bangare ne na kokarin magance matsalar rashin isassun tantuna da aka ware wa alhazan Najeriya a Muna.

 Ya bayyana cewa matakin ya biyo bayan korafin da NAHCON ta kai wa Muttawwif na Alhazai na kasashen Larabawa kan rashin isassun tantuna, rashin wadataccen abinci, da kuma karancin abinci ga maniyyatan.

 Muttawwif yayin da ya ke ba da hakuri kan yadda aka yi wa mahajjatan Najeriya, ya yi alkawarin mayar da alhazan zuwa sansanin kasar Turkiyya wanda zai iya daukar kimanin mahajjata 10,000 cikin sauki.

By/Daga - Click/Latsa isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN