Daga karshe: Dalilai sun bayyana da ya sa Tinubu ya dakatar da shugaban EFCC Abdulrasheed Bawa


An dakatar da Mista AbdulRasheed Bawa, Shugaban Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (EFCC) daga aiki har zuwa wani lokaci.

 Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ne ya bayar da umarnin dakatar da shi biyo bayan wasu zarge-zargen cin zarafi na ofis. PM News ya rahoto.

 A cikin wata sanarwa da ofishin sakataren gwamnatin tarayya ya fitar, shugaban ya ba da umarnin dakatar da Bawa don ba da damar gudanar da bincike mai kyau a kan yadda ya ke aiki a lokacin da yake kan mulki.

 Akwai manyan zarge-zarge da dama a kan sa na cin hanci da rashawa, ciki har da zargin da tsohon gwamnan Zamfara, Bello Matawalle ya yi.

 Ya yi ikirarin cewa Bawa ya bukaci dala miliyan 2 daga gare shi kuma ya sa mutumin a kaset.

 Akwai kuma zarge-zarge masu tsanani na cin zarafin ofishin da aka yi masa.

 Willie Bassey, Daraktan Yada Labarai ya ce an umurci Bawa da ya gaggauta mika ayyukan ofishinsa ga Daraktan Ayyuka a Hukumar.

 Daraktan zai kula da harkokin ofishin shugaban hukumar har sai an kammala bincike.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN