Ba sulhu tsakanin mu da Yan bindiga, za mu bi su har daji mu ..Gwamnan Zamfara


Gwamnatin jihar Zamfara a ranar Talata ta ce ba za su taba shiga tattaunawar zaman lafiya ba ko kuma su shiga cikin wata tattaunawa da ‘yan bindiga a jihar. Daily trust ta rahoto.

 Da yake zantawa da manema labarai a garin Gusau sakataren gwamnatin jihar Alhaji Abubakar Nakwada ya ce gwamnati mai ci ba ta da niyyar shigar da duk wani shugaban ‘yan bindiga ko wakilinsu a tattauna komi, da sunan yarjejeniyar zaman lafiya. 

 Nakwada ya bayyana shirin gwamnatin jihar na, maimakon haka, ta bi ‘yan bindigar zuwa duk inda suke tare da murkushe su ciki har da masu daukar nauyinsu.

 Ya ci gaba da cewa gwamnatin jihar za ta yi aiki tukuru tare da hadin gwiwar jami’an tsaro don ganin an kai ga yaki da rashin tsaro.

By/Daga - Click/Latsa isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN