An samu gobarar fashewar gidan sayar da iskar gas a garin Azare

AN SAMU GOBARAR FASHEWAR GIDAN SAYAR DA  ISKAR GAS A AZARE 

Daga Muazu Hardawa Bauchi

An samu gobarar fashewar gidan sayar da iskar gas a garin Azare
Illustrative please

An samu gobarar fashewar takwanen iskar gas a wani gidan sai da gas na girki da ke kan hanyar zuwa Misau a cikin garin Azare da ke Jihar Bauchi a safiyar wannan litinin, sai ko har zuwa yanzu ba'a san dalilin tashin gobarar ba.

 Amma wani mazaunin garin da lamarin ya abku kan idon sa, Malam Kamal Ahmed ya ce babu asarar rayuwa ko rauni saiko asarar dukiya. Yace Jami'an kashe gobara da jami'an tsaro sun halarci wurin ba tare da bata lokaci ba don kai dauki kuma an yi nasarar kashe wutar.

Mamallakin wurin mai suna Alhaji Kawu tun farko ya jima da bude wannan wajen sayar da iskar gas a kusa da tashar Mota ta hanyar zuwa Misau. 

Amma ganin irin hatsarin da ke tattare da wannan sana'a sai gwamnati ta fitar da shi daga inda yake zuwa wajen gari kuma ya kawatar da wajen bisa yadda doka ke so, ya ci gaba da harkar har lokacin da wannan tsautsayi ya abku a wajen.

Dukkan kokarin da muka yi don jin ta bakin mamallakin wurin da hukumomin tsaro ya ci tura sai ko nan gaba idan mun ji ta bakin su za mu sanar da masu karatu.

By/Daga - Click/Latsa isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN