Type Here to Get Search Results !

Yanzu yanzu: Bayan kunyata jam'iyar LP sakamakon yin fada a Kotun sauraren karakin zabe, NLC ta yi watsi da Lamidi Apapa


Kungiyar kwadago ta Najeriya NLC ta yi watsi da shugaban jam’iyyar Lamidi Apapa
.


 A wata sanarwa da Chris Uyoh, sakataren NLC ta kasa ya fitar, kungiyar kwadago ta yi Allah wadai da matakin da Lamidi ya dauka a kotun zaben shugaban kasa a ranar Laraba, 17 ga watan Mayu, inda ta bayyana hakan a matsayin abin kunya.  Kungiyar ta bayyana cewa abin takaici ne yadda Apapa, ke bayyana wa kansa "wani matsayi mara kyau a matsayin shugaban jam'iyyar Labour."


Ufot ya ce jam'iyyar Labour wadda NLC ta kafa fiye da shekaru talatin da suka gabata, ta samar da mambobi na hukumomi ga NLC da Trade Union Congress (TUC).


Kungiyar ta NLC ta ce, matakin da Mista Lamidi Apapa da tawagarsa suka dauka na nuna shakku kan yadda wasu masu sha'awar siyasa a Najeriya suka ci gaba da yin hakan, wadanda fatansu shi ne mutuwar jam'iyyar Labour.


Post a Comment

0 Comments
* Please Don't Spam Here. All the Comments are Reviewed by Admin.

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN