Tinubu Ya Gana Da Kwankwaso a Paris Kan Batun Shigowarsa Cikin Gwamnatinsa


Zaɓaɓɓen shugaban ƙasa Bola Tinubu na APC ya yi wani zama da Rabiu Musa Kwankwaso na jam'iyyar NNPP a birnin Paris da ke ƙasar Faransa.

Tattaunawar dai ta gudana ne a ranar Litinin da ta gabata, tsakanin Bola Tinubu da Kwankwaso, wacce ta É—auke su tsawon sa'o'i hudu. Legit ya wallafa.

Tinubu ya ce yana shirin kafa “gwamnatin haÉ—in kan 'yan Æ™asa” wacce za ta haÉ—a da ‘yan jam’iyyun adawa, dalilin Tinubu da rahotanni suka bayyana na zama da Kwankwason kenan.

Mutanen biyu sun kuma tattauna batun zaÉ“en shugabannin majalisar dokokin Æ™asar da ke tafe. Jam’iyyar APC ta bayyana mutanen da ta ke so su jagoranci tagwayen majalisun.

Sai dai wasu ‘ya’yan jam’iyyar APC na adawa da wannan tsari kuma sun yi barazanar sauya sheÆ™a zuwa jam’iyyar adawa idan har ba a sauya tsarin ba.

Jam'iyyar NNPP na da Sanatoci biyu da 'yan majalisar wakilai 19. Idan har waÉ—annan ‘ya’yan jam’iyyar za su haÉ—a Æ™arfi da Æ™arfe da ‘yan adawa, za su iya hana jam’iyyar APC samun rinjaye a yayin zaÉ“en.

Wadanda suka halarci ganawar baya ga Kwankwaso

Ganawar tsakanin Tinubu da Kwankwaso ta samu halartar Femi Gbajabiamila, kakakin majalisar wakilai kuma shugaban ma’aikatan fadar shugaban Æ™asa mai jiran gado.

Abdulmumin Jibrin, dan majalisar wakilai na NNPP kuma tsohon jigo a kungiyar yaƙin neman zaɓen Tinubu, shi ma ya samu halarta.

Oluremi Tinubu, uwargidan shugaban ƙasa, ta karbi Salamatu Kwankwaso, matar Rabiu Musa Kwankwaso.

Rahotanni sun bayyana cewa mutanen biyu sun tuno da irin dangantakarsu da ta samo asali tun a shekarar 1992. A wancan lokacin Tinubu ya kasance Sanata ne, Kwankwaso kuma shi ne mataimakin kakakin majalisar wakilai.

Kwankwaso ya ce zai yi shawara da mutanensa

The Cable ta ce Kwankwaso ya ce zai tattauna da masu ruwa da tsaki a bangarorin biyu domin jin ta bakinsu kafin ya amince.

Ana sa ran Tinubu zai yi wa Kashim Shettima, da kungiyar gwamnonin APC, da sauran shugabannin jam’iyyar bayani, a yayin da shi ma Kwankwason zai yi haka ga shugabancin jam’iyyarsa.

Tinubu ya nuna damuwarsa kan alaƙar Kwankwaso da Ganduje

Tinubu ya kuma bayyana damuwarsa kan yadda dangantaka ta yi tsami tsakanin Abdullahi Ganduje, gwamnan jihar Kano mai barin gado da Kwankwaso.

Ganduje ya kasance mataimaki ga Kwankwaso a lokacin yana gwamnan Kano daga 2011 zuwa 2015, kafin rabuwarsu.

Yanzu dai jama'a sun zura ido, suna jiran su ga ko Kwankwaso zai aminta da tayin shiga gwamnatin Tinubun ko a'a.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN