Da duminsa: Yan bindiga sun kashe mutum 40 a Kebbi da Zamfara



Akalla mutum 40 ne ’yan bindiga suka kashe, ciki har da jami’an tsaro, a jihohin Kebbi da Zamfara a ranar Lahadi.

Daga cikin mutanen da aka kashe har da ’yan sandan kwantar da tarzoma shida da fararen hula 36 a kauyen Dan Umaru da ke Karamar Hukumar Damko Wasagu a Masarautar Zuru a Jihar Kebbi. Jaridar Aminiya ta wallafa.

Mazauna yankin sun shaida wa wakilinmu cewa an gudanar da jana’izar mutum 27, wasu mutane da dama kuma sun samu raunuka a harin.

Sun bayyana cewa maharan sun kuma sace mutane da daruruwan dabbobi a kauyukan da ke makwabtaka da su.

A Jihar Zamfara kuma an kashe wasu mutum uku a wani kauye da ke Karamar Hukumar Shinkafi.

Sai dai har zuwa lokacin da muka kammala rubuta wanann labarin, hukumomin ’yan sanda ba su fiar ta bayani kan lamarin ba.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN