Type Here to Get Search Results !

Da duminsa: Yan bindiga sun kashe mutum 40 a Kebbi da Zamfara



Akalla mutum 40 ne ’yan bindiga suka kashe, ciki har da jami’an tsaro, a jihohin Kebbi da Zamfara a ranar Lahadi.

Daga cikin mutanen da aka kashe har da ’yan sandan kwantar da tarzoma shida da fararen hula 36 a kauyen Dan Umaru da ke Karamar Hukumar Damko Wasagu a Masarautar Zuru a Jihar Kebbi. Jaridar Aminiya ta wallafa.

Mazauna yankin sun shaida wa wakilinmu cewa an gudanar da jana’izar mutum 27, wasu mutane da dama kuma sun samu raunuka a harin.

Sun bayyana cewa maharan sun kuma sace mutane da daruruwan dabbobi a kauyukan da ke makwabtaka da su.

A Jihar Zamfara kuma an kashe wasu mutum uku a wani kauye da ke Karamar Hukumar Shinkafi.

Sai dai har zuwa lokacin da muka kammala rubuta wanann labarin, hukumomin ’yan sanda ba su fiar ta bayani kan lamarin ba.

Post a Comment

0 Comments
* Please Don't Spam Here. All the Comments are Reviewed by Admin.

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN