Type Here to Get Search Results !

Main event

Yan bindiga sun kashe Yan sandan kwantar da tarzoma 6 da mutane 30 a kauyukan Masarautar Zuru jihar Kebbi


Wasu ‘yan bindiga sun kashe ‘yan sandan kwantar da tarzoma Mopol 6 da wasu mutane 30 a kauyen Dan Umaru da ke karamar hukumar Danok Wasagu a yankin Masarautar Zuru a jihar Kebbi.

 An kai harin ne da sanyin safiyar Lahadi, 30 ga Afrilu, 2023.

 An kuma yi garkuwa da mutane da dama tare da sace daruruwan shanu yayin harin da aka kai kauyukan da ke makwabtaka da su.

 Kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito, mazauna garin sun ce an yi jana'izar mutane 27 yayin da wasu da dama suka samu raunuka daban-daban.

 Har yanzu dai hukumomin ‘yan sanda a jihar ba su bayar da wata sanarwa a hukumance kan harin ba har ya zuwa lokacin gabatar da wannan rahoto.

 A halin da ake ciki dai, abokai da 'yan uwa da abokan aiki sun yi ta yada hotunan jami'an 'yan sandan da aka kashe a shafukan sada zumunta. Yayin da suke masu addu'a da jajenta wa iyalansu.

Post a Comment

0 Comments
* Please Don't Spam Here. All the Comments are Reviewed by Admin.

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN

Hollywood Movies