An tsinci yarinyar wacce take shekara biyu a fannin zane-zane a Jami'a a rataye a wani fanfo a gidanta a ranar Lahadi, 7 ga Mayu.
Matashiyar ta bayyana a cikin bayanin kashe da ta rubuta cewa ita Yar madigo ce. Matar ta ci gaba da cewa ba zai yiwu ta auri namiji ba kuma ta yi rayuwa mai dadi.
Yarinyar ta kuma bayyana a cikin bayanin nata na kashe cewa zabin kashe rayuwarta ta hanyar kashe kanta ya zama abin farin ciki a gare ta fiye da yadda ta rungumi salon rayuwar da ba ta so.
Ta baiwa iyayenta hakuri akan abinda ta aikata a cikin takardar. Bayan da ta kashe kanta, an gudanar da gwaji a gawarta a ranar Litinin, inda aka mika gawar ta ga iyayenta domin yin ibada ta karshe. Daga nan suka kai ta kauyensu domin yi mata jana'iza.
Lamarin dai ya tayar da tarzoma a tsakanin ‘yan madigo.
‘Yan sandan sun ce matashiyar ta gaza samun tallafi daga wajen iyayenta bayan sun gano ita ‘yar madigo ce. Yayin da iyayen suka ki amincewa da abubuwan da take so na jinsi, ita ma ta ki amincewa, in ji wani babban sifeta Nitin Vithole daga ofishin 'yan sanda na Gittikhadan, wanda ya ziyarci wurin da budurwar ta kashe kansa.
“Budurwar ta É—auki mataki mai tsauri lokacin da dangin ba su nan. Mahaifin shi ne ya fara ganin gawarta da aka rataye,” in ji Vithole.
BY ISYAKU.COM
RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI