An zartar da dokar rage makudan kudade da ake kashewa a auratayya, suna, kaciya da sauran bukukuwa a jihar Sokoto


Majalisar dokokin jihar Sokoto a ranar Talata ta zartas da wani kudiri na daidaita kudaden aure a jihar. NAN ya ruwaito.

 Kudurin dokar wanda Alhaji Abubakar Shehu (APC-Yabo) da Faruk Balle (PDP- Gudu) suka dauki nauyinsa, an mika shi ga kwamitin kula da harkokin addini na majalisar.

 Shehu, wanda shi ne Shugaban kwamitin, ya gabatar da rahoton kwamitin a zauren taron, wanda aka amince da shi gaba daya ya zama doka.

 Kudirin ya nemi a kula da yadda ake kashe makudan kudade a auratayya, suna, kaciya da sauran bukukuwan gida a fadin jihar.

 Shehu ya ce yayin da yake gabatar da rahoton, kwamitin ya gana da masu ruwa da tsaki wadanda suka bayar da gudunmawa mai kyau, wadanda aka saka a cikin kudirin dokar.

 Bayan tattaunawa a zaman da mataimakin shugaban majalisar, Alhaji Abubakar Magaji ya jagoranta, ‘yan majalisar sun amince da kudurin gaba daya nan take da gagarumin rinjaye. .

1 Comments

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

  1. gaskiya abin yayi daidai Allah shi biya majalisa da ta bada wannan kudirin kuma suka samai hannu kuma Allah shi sa sau ran garuruwan Arewa su kyai kyayesu

    ReplyDelete
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN