Yanzu yanzu: Soja ya harbi barawon akwatin zabe a Kebbi


Soja ya dirka wa wani mutum harbi a yayin da mutumin ya yi yunkurin kwace akwatin zabe daga hannun jami'an INEC a Karamar Hukumar Fakai ta Jihar Kebbi. Jaridar Aminiya ta ruwaito.

Shaidu sun ce wanda aka harba din tsohon dan haramtacciyar kungiyar tsaro ta sa-kai ne wanda shi da abokansa suka kutsa wata rumfar zabe a matsayin jami'an tsaro.

A nan ne suka yi yunkurin kwace akwatin zabe a hannun jami'an INEC, kuma kokarin mutanen wurin na hana su ya ci tura.

An ce ya yi yunkurin kwace bindiga a hannun wani soja, shi ne sojan ya dirka mishi harbi.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN