Type Here to Get Search Results !

An kashe almajiri an kwakule idonsa a Jigawa cikin watan Azumi


Wasu da ba san ko su wane ne ba sun kashe wani almajiri sannan suka kwakule idonsa a Jihar Jigawa.

An tsinci gawar ce bayan an jima ana neman shi, kafin daga bisa aka tsinci gawarsa kwance cikin jini an kwakule masa ido daya. Jaridar Aminiya ta ruwaito.

Rundunar ’yan sandan jihar ta ce kafin a gano gawar, malamin almajirin ya kai rahoto caji ofis cewa tun da yaron ya je neman ice ba a sake jin duriyarsa ba.

Kakakin rundunar, Lawal Shiisu, ya ce malamin mai suna Malam Muhammad Mustafa, “ya yi mana korafi tun da misalin karfe 8 na safiyar Juma’a wani almajirinsa ya tafi nemo ice amma bai dawo gida ba.

“Daga baya aka tsinci gawar almajirin an kwakule masa ido daya,” a kai ta Babban Asibitin Dutse inda likita ya tabbatar ya rasu.

A cewar Shiisu, rundunar ’yan sandan ta fara farautar wadanda suka yi wannan aika-aika.

Post a Comment

0 Comments
* Please Don't Spam Here. All the Comments are Reviewed by Admin.

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN